Ƴan bindiga sun sace ɗaliban Jami’ar Tarayya ta Gusau

Posted admin News 331 Views 2 Min Read
2 Min Read

Bayanai daga jihar Zamfara a arewa maso yammacin Najeriya na cewa wasu ƴan bindiga sun kai hari a gidajen kwanan ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau, tare da sace ɗalibai waɗanda har yanzu ba a tantance adadinsu ba.

Lamarin dai ya faru ne da asubahin ranar Juma’a, inda rahotanni ke cewa maharan sun kutsa gidajen kwanan ɗalibai guda uku a unguwar Sabon Gida da ke mawaftaka da jami’ar.

Bayanan na cewa ƴan bindigar sun samu nasarar kwashe kusan dukkanin ɗaliban da ke zaune a gidajen waɗanda ke daura da jami’ar.

Har yanzu dai hukumomi ba su yi ƙarin bayani kan lamarin ba.

Zamfara na daga cikin jihohin da suka fi jigata daga ayyukan ƴan bindiga masu fashi da kuma garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa.

Ko a cikin watan Fabarairun 2021, ƴan bindiga sun shiga makarantar sakandare ta GGSS Jangebe a jihar, inda suka sace ɗalibai mata 317.

Haka nan ma a baya-bayan nan ƴan bindiga sun kai hari a wasu ƙauyukan jihar inda suka kashe mutane da dama tare da sace ƴan mata fiye da 30 a ƙaramar hukumar Maradun.

Maharan sun abka ƙauyukan Sakkiɗa da Janbako da rana tsaka, inda suka kashe mutum sama da 20 a Sakkiɗa tare da jikkata karin wasu.

Ita dai gwamnatin jihar ƙarƙashin gwamna Dauda Lawal, ta ce tana ɗaukar duk matakan da suka dace wajen shawo kan lamarin, sai dai ta sha alwashin cewa ba za ta taɓa yin sulhu da ƴan bindiga ba.

A baya dai gwamnatocin da suka gabata a jihar sun ɗauki matakai daban-daban, ciki har da na yarjejeniya da ƴan bindigar, sai dai har yanzu matsalar ta ci tura.

BBC Hausa

Share this Article
Posted by admin
Follow:
A group of seasoned crime reporters drawn from reputable media organisations in Nigeria. To help in creating a friendly Nigerian Police Force that meets the yearnings and aspirations of the citizens towards policing and security of lives and properties. To showcase the positive sides of the Force, as well as celebrating the great feat of police personnel, who have shown uncommon courage in the discharge of his / her responsibility. In the same vein, through objective ratiocination, identify the areas of shortcomings for corrections. We welcome you on board on this journey to build an enviable Nigeria Police Force by actively playing the role of a watch dog. Watch out for crime stories and other security titbits.
Leave a comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *