Babu dokar da ta ce sai na gama NYSC za a naɗa ni minista – Hannatu Musawa

Posted admin Arewa & Kai 330 Views 1 Min Read
1 Min Read

Ministar Al’adu ta Najeriya Hannatu Musawa ta musanta zargin da ake yi mata na karya dokar ƙasa bayan naɗa ta a muƙamin duk da cewa ba ta kammala hidimar ƙasa ta NYSC ba.

Cikin wani martani da ta fitar a yau Lahadi, ministar ‘yar jihar Katsina a arewacin Najeriya ta ce “babu wata doka da na karya”.

“Dole ne na faɗa cewa babu wata doka a Najeriya da ta ce shugaban ƙasa ko wata hukuma ba za su iya naɗa mutumin da yake hidimar ƙasa a muƙami na siyasa ba,” in ji ta.

Sai dai, mai magana da yawun hukumar National Youth Service Commission (NYSC), Eddy Megwa, ya faɗa wa Daily Trust cewa “ta karya doka kuma muna duba yiwuwar ɗaukar matakin da ya dace” a kanta.

A ranar Litinin 21 ga watan Agusta Shugaba Bola Tinubu ya rantsar da Hannatu – wadda yanzu haka take gudanar da hidimar ƙasar a Abuja – a matsayin minista tare da sauran mutum 45.

Hannatu ta tabbatar da cewa tun a 2001 aka tura ta hidimar ƙasar zuwa jihar Akwa Ibom amma ta ɗage aiwatarwa sai a 2023 ta ci gaba.

Credit: BBC Hausa

Share this Article
Posted by admin
Follow:
A group of seasoned crime reporters drawn from reputable media organisations in Nigeria. To help in creating a friendly Nigerian Police Force that meets the yearnings and aspirations of the citizens towards policing and security of lives and properties. To showcase the positive sides of the Force, as well as celebrating the great feat of police personnel, who have shown uncommon courage in the discharge of his / her responsibility. In the same vein, through objective ratiocination, identify the areas of shortcomings for corrections. We welcome you on board on this journey to build an enviable Nigeria Police Force by actively playing the role of a watch dog. Watch out for crime stories and other security titbits.
Leave a comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *