Tsagin jam’iyyar NNPP ta kasa bangaren Major Agbo, ya dakatar da dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar a zaben da ya gabata, Rabi’u Musa Kwankwaso, saboda zargin cin amanarta.
Jam’iyyar ta kuma zargi Kwankwason da karkatar da kudaden yakin neman zabenta.